Skip to main content

Wato tazarar da'awar Dr. DT ta matuqar shan banban da ta Sheikh Albani (Ra) musamman a wannan datsin, wayewar su da mu'amala ba daya bane.

Yanzu nake ganin wata sanarwa ta neman shi ido rufe daga ofishin shugaban yan sanda na Bauchi da Gomnatin ta.

Naji ba dadi ganin hakan in gaskiya ne, kuma abin takaici ne, sai dai da yawa almajirai suke janyo irin matsalar nan da mashawarta.


Sheikh Albani yayi rikici da Gomnati sosai a lokacin sa, kuma shine yake nasara, duba da yasan Shari'a, yasan doka dai dai gwargwado, ga wayewa ga bin abubuwa sannu a hankali wajen mu'amalantar wanda suka saba dashi bakin iyawan shi, musamman a karshe karshen da'awar shi a duniya.


Abin burgewa daliban da Sheikh Albani ya gamsu dasu a matsayin dalibai da abokai, basa yin hargowa a komai domin wayewar su da kuma tarbiyyar da ya masu.


Amma shi DT matsalar rikicinsa da kowa da rushe duk abinda gomnati ya yarda dasu a matsayin dai dai kun mutane da kuma Kungiyoyi da Jagorori, wanda Sheikh Albani har Jam'iyya yana da ita ba iya Kungiya ba, ko a iya baki ne duk wadanda ya jinginu dasu zasu ji dadi kuma in abu ya taso zasu tsayu akan lamarin.


Shi kuma DT ba ruwan shi da kowa, musamman dattijai da masu hankalin gaban shi, sai wasu yara da yan media da masu bashi gurguwar shawara yake bi, tsakani ga Allah bama jin dadin rikicin malamai da malamai, balle muga yan siyasa zasu ci zarafin mai addini koda mun saba a manhaji da matsotsar addini.


Koma dai menene fatan mu Allah ya gyatta lamuran mu dashi ya bamu mafita dashi da sauran yan uwa ya shiryar damu ya tsaremu daga afkawa cikin mummunan kaddara don tsarkin sunayen ka.

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Kuskuren Farko da Tinubu Yayi Ya Jefa Mutanen Najeriya a Wahala.

Tsohon shugaban PACAC, Itse Sagay ya soki gaggawan janye tallafin man fetur da aka yi a bara Farfesan yana gani kyau sabon shugaban Najeriya ya jira sai matatun cikin gida sun fara aiki tukun Itse Sagay yana sa ran gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kawo sauyin al’amura a Najeriya  - Itse Sagay Farfesa ne kuma babban lauya a Najeriya, ya soki tsarin janye tallafin man fetur da aka tabbatar da shi a 2023. A wata zantawa da tashar Channels tayi da shi, Farfesa Itse Sagay ya yi tir da da Bola Tinubu a kan daina biyan tallafin man fetur.  Itse Sagay ya bada misali da matatar Aliko Dangote da ta gwamnati da ke Fatakwal, ya so ina ma sun fara aiki kafin fetur ya tashi. Itse Sagay bai ji dadin tashin fetur ba "Fetur yana da muhimmanci a rayuwarmu.  Tsadar rayuwa ta na ta karuwa kuma rayuwa tayi kunci. Ina tunani ya kamata a ce mun jira na watanni shida domin za a fara tace mai a gida, sai a cire tallafi. Gaggawa da yadda aka janye tallafin nan ta ke ya kirkiro wahalar...

Abubuwan da suka haifar wa duniya tsadar Rayuwa

Tsadar rayuwa wata matsala ce da ke neman zame wa duniya wata babbar barazana. Inda ƙasashen duniya da dama ke cikin wannan matsala, sakamakon tashin farashin abubuwan amfani na yau-da-kullum. A baya-bayan nan Najeriya da sauran ƙasashen Afirka irinsu Ghana da Nijar na fuskantar matsalar tsadar rayuwa. To sai dai matsalar ba ta tsaya ga nahiyar Afirka kaɗai ba, al'amari ne da ya shafi duniya baƙi-ɗaya. Shin me ke haifar da wannan matsala da tsadar rayuwa a faɗin duniya? 1-Tashin farashin makamashi da man fetur An samu ƙaruwar farashin man fetur tun bayan ɓarkewar annobar korona, inda buƙatar man fetur ɗin ta ƙaruwa a duniya sakamakon matakin kullen korona da ƙashen duniya da dama suka ɗauka. Wannan abu ya sa man fetur ɗin ya kai tsadar da bai taɓa kai wa ba cikin shekaru masu yawa. A yanzu dai ana sayar da gangar ɗanyen mai man fetur kan dala 79 zuwa sama a kasuwannin duniya. Hakan ya faru ne sakamakon yaƙin Ukraine da Rasha, Ita dai Rasha na cikin ƙasashen da suke da arzikin man f...