Skip to main content

Wato tazarar da'awar Dr. DT ta matuqar shan banban da ta Sheikh Albani (Ra) musamman a wannan datsin, wayewar su da mu'amala ba daya bane.

Yanzu nake ganin wata sanarwa ta neman shi ido rufe daga ofishin shugaban yan sanda na Bauchi da Gomnatin ta.

Naji ba dadi ganin hakan in gaskiya ne, kuma abin takaici ne, sai dai da yawa almajirai suke janyo irin matsalar nan da mashawarta.


Sheikh Albani yayi rikici da Gomnati sosai a lokacin sa, kuma shine yake nasara, duba da yasan Shari'a, yasan doka dai dai gwargwado, ga wayewa ga bin abubuwa sannu a hankali wajen mu'amalantar wanda suka saba dashi bakin iyawan shi, musamman a karshe karshen da'awar shi a duniya.


Abin burgewa daliban da Sheikh Albani ya gamsu dasu a matsayin dalibai da abokai, basa yin hargowa a komai domin wayewar su da kuma tarbiyyar da ya masu.


Amma shi DT matsalar rikicinsa da kowa da rushe duk abinda gomnati ya yarda dasu a matsayin dai dai kun mutane da kuma Kungiyoyi da Jagorori, wanda Sheikh Albani har Jam'iyya yana da ita ba iya Kungiya ba, ko a iya baki ne duk wadanda ya jinginu dasu zasu ji dadi kuma in abu ya taso zasu tsayu akan lamarin.


Shi kuma DT ba ruwan shi da kowa, musamman dattijai da masu hankalin gaban shi, sai wasu yara da yan media da masu bashi gurguwar shawara yake bi, tsakani ga Allah bama jin dadin rikicin malamai da malamai, balle muga yan siyasa zasu ci zarafin mai addini koda mun saba a manhaji da matsotsar addini.


Koma dai menene fatan mu Allah ya gyatta lamuran mu dashi ya bamu mafita dashi da sauran yan uwa ya shiryar damu ya tsaremu daga afkawa cikin mummunan kaddara don tsarkin sunayen ka.

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Ko shigar da abinci Najeriya zai samar da mafita ga tsadar rayuwa?

A ke ciki sannan dan kasuwa shi ma yana fuskantar koma-bayan ciniki saboda mutane na fama wajen samun kudin da za su shiga kasuwa. Ya ce tsugunu ba ta kare ba a damar da gwamnati ta bayar na ba da dala ga duk mai son shigar da abinci daga wasu kasashen kasancewar dalar ta yi karanci a babban bankin Najeriya. "Domin duk wanda zai siyo abinci a waje, ko dai ya canza naira zuwa dala, ko naira zuwa CFA, ko zuwa me ka canza naira, idan ka siyo abincin ba za ka sayar da shi a kan sauki ba." in ji Dr Kani. Dr Muhammad Suleiman Kani ya ce matukar gwamnati na son kawo sauki toh kamata ya yi gwamnati ta haramta shigar da duk kayan da za a iya samu a Najeriya. A cewarsa, idan gwamnati ta dauki wannan mataki, ya kamata ta hanzarta tayar da komadar kamfanoni da wutar lantarki domin su tsaya da kafafunsu. Ya kuma yi kira ga shugaban kasa ya tashi tsaye wajen yin abin da ya dace domin fitar da Najeriya daga kangin da take ciki. A cewar masanin, ya kamata gwamnati ta cika alkawur...

Kuskuren Farko da Tinubu Yayi Ya Jefa Mutanen Najeriya a Wahala.

Tsohon shugaban PACAC, Itse Sagay ya soki gaggawan janye tallafin man fetur da aka yi a bara Farfesan yana gani kyau sabon shugaban Najeriya ya jira sai matatun cikin gida sun fara aiki tukun Itse Sagay yana sa ran gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kawo sauyin al’amura a Najeriya  - Itse Sagay Farfesa ne kuma babban lauya a Najeriya, ya soki tsarin janye tallafin man fetur da aka tabbatar da shi a 2023. A wata zantawa da tashar Channels tayi da shi, Farfesa Itse Sagay ya yi tir da da Bola Tinubu a kan daina biyan tallafin man fetur.  Itse Sagay ya bada misali da matatar Aliko Dangote da ta gwamnati da ke Fatakwal, ya so ina ma sun fara aiki kafin fetur ya tashi. Itse Sagay bai ji dadin tashin fetur ba "Fetur yana da muhimmanci a rayuwarmu.  Tsadar rayuwa ta na ta karuwa kuma rayuwa tayi kunci. Ina tunani ya kamata a ce mun jira na watanni shida domin za a fara tace mai a gida, sai a cire tallafi. Gaggawa da yadda aka janye tallafin nan ta ke ya kirkiro wahalar...