Skip to main content

Ko shigar da abinci Najeriya zai samar da mafita ga tsadar rayuwa?

Ake ciki sannan dan kasuwa shi ma yana fuskantar koma-bayan ciniki saboda mutane na fama wajen samun kudin da za su shiga kasuwa.

Ya ce tsugunu ba ta kare ba a damar da gwamnati ta bayar na ba da dala ga duk mai son shigar da abinci daga wasu kasashen kasancewar dalar ta yi karanci a babban bankin Najeriya.

"Domin duk wanda zai siyo abinci a waje, ko dai ya canza naira zuwa dala, ko naira zuwa CFA, ko zuwa me ka canza naira, idan ka siyo abincin ba za ka sayar da shi a kan sauki ba." in ji Dr Kani.

Dr Muhammad Suleiman Kani ya ce matukar gwamnati na son kawo sauki toh kamata ya yi gwamnati ta haramta shigar da duk kayan da za a iya samu a Najeriya.

A cewarsa, idan gwamnati ta dauki wannan mataki, ya kamata ta hanzarta tayar da komadar kamfanoni da wutar lantarki domin su tsaya da kafafunsu.

Ya kuma yi kira ga shugaban kasa ya tashi tsaye wajen yin abin da ya dace domin fitar da Najeriya daga kangin da take ciki.

A cewar masanin, ya kamata gwamnati ta cika alkawuran da ta daukar wa jama'a bayan janye tallafin man fetur na kara albashi da inganta walwalar al'umma da tayar matatar mai ta Fatakwal.

A cewar kwararren kan samar da abinci, tsarin shigar da abinci daga wasu kasashen hanya ce mai kyau sai dai akwai bukatar gwamnati ta sa ido domin tabbatar da cewa tsarin ya tafi sumul kalau ga amfanin yan kasa.

Ya ce "dole hukumomin tsaro su sa ido saboda dabi'ar yan Najeriya, za a iya shigar da kayan abincin sai ka ga wasu tsirarun mutane sun debe abincin an sauya buhu, sun kai shi kasuwa ana kuma cinikinsa."

Ya kuma ce bai kamata gwamnati ta sake kuskuren bayar da abincin ta hannun gwamnoni ba, kasancewar irin wannan tsarin a baya, bai yi nasara ba.

Dr Kani ya ce a yi amfani da kasuwannin da ake da su da kuma cibiyoyin gwamnati na harkar abinci, sannan a yi tsarin a bude, "babu maganar gwamnoni ko yan majalisa."

Ya ce gwamnati ta aiwatar da abin da kanta sannan ta saka yan farar hula da za su sa ido kan yadda tsarin ke tafiya domin tabbatar da an yi shi bisa gaskiya.

Dr Muhammad Kani ya bayyana cewa tsarin na gwamnati zai iya shafar harkokin yan kasuwa inda ya ce a wasu kasashe kamar Amurka gwamnati tana siyan kayan abinci sai ta rage farashinsu a duk lokacin da aka gama harkokin noma.

Ya ce tsarin bai tsaya iya nan ba, Saudiyya ma tana aiwatar da irin tsarin.

"A Saudiyya, akwai lokacin da idan kaya suka yi yawa sai ta gayyato manoma, ta ce kada su yi noma," tana tambayar nawa ce ribarsu sai ta dauki ribar ta basu.

"Saboda idan ya yi yawa ya wuce hankali za a yi asara, za ku noma ba ku ci riba ba." kamar yadda ya ce.

A cewar masanin, daukan wannan tsarin zai kawo gasa kuma zai sa wadanda suke samar da abin na cikin gida suma su karyar da farashin kayansu.

Masanin ya ce rashin isassun rumbuna ka iya kawo tarnaki ga matakin shigo da kayan abincin saboda rashin tanadin wuraren da za a ajiye su wanda hakan zai iya jawo lalacewarsu.

Ya kuma a yanzu gwamnatin ba ta da kayan abincin a kasa, a yanzu ne za ta shigo da su kuma abin tambayar a cewarsa shi ne da wane kudi za ta siyo kayan?

Ya ce ma'ana dole sai gwamnati ta ciwo bashi domin sayo kayan abincin.

AMH Hausa 

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Abubuwan da suka haifar wa duniya tsadar Rayuwa

Tsadar rayuwa wata matsala ce da ke neman zame wa duniya wata babbar barazana. Inda ƙasashen duniya da dama ke cikin wannan matsala, sakamakon tashin farashin abubuwan amfani na yau-da-kullum. A baya-bayan nan Najeriya da sauran ƙasashen Afirka irinsu Ghana da Nijar na fuskantar matsalar tsadar rayuwa. To sai dai matsalar ba ta tsaya ga nahiyar Afirka kaɗai ba, al'amari ne da ya shafi duniya baƙi-ɗaya. Shin me ke haifar da wannan matsala da tsadar rayuwa a faɗin duniya? 1-Tashin farashin makamashi da man fetur An samu ƙaruwar farashin man fetur tun bayan ɓarkewar annobar korona, inda buƙatar man fetur ɗin ta ƙaruwa a duniya sakamakon matakin kullen korona da ƙashen duniya da dama suka ɗauka. Wannan abu ya sa man fetur ɗin ya kai tsadar da bai taɓa kai wa ba cikin shekaru masu yawa. A yanzu dai ana sayar da gangar ɗanyen mai man fetur kan dala 79 zuwa sama a kasuwannin duniya. Hakan ya faru ne sakamakon yaƙin Ukraine da Rasha, Ita dai Rasha na cikin ƙasashen da suke da arzikin man f...

Jihohin arewacin Najeriya bakwai da za su fuskanci yunwa

-Bankin Duniya A wani rahoto da bankin na duniya ya wallafa tun ranar 1 ga watan Fabrairu kuma ya samu watsuwa a ranar 8 ga watan na Fabrairu ya fitar da bayan na sassan duniya da matsalolin yunwa da za su fuskanta. A sashen Afirka ta yamma da ta tsakiya, rahoton mai taken 'Food Security Update 2024', ya bayyana cewa wasu jihohi guda bakwai na arewa maso yammaci da gabashi da wadanda za su fuskanci matsalar yunwa tun daga farkon shekarar nan har zuwa watan Mayu. Jihohin dai su ne: Adamawa Borno Kaduna Katsina Sokoto Yobe Zamfara. Rahoton dai ya bayyana dalilan rashin tsaro na 'yan bindiga da ke satar jama'a a jihohi kamar Kaduna da Katsina da Sokoto da Zamfara, inda su kuma Borno da Yobe da Adamawa ke fuskantar matsalar Boko Haram. Harwayau, rahoton ya yi wa jihohin kudin goro da sauran sassan Najeriya da ke fama da matsalar tsadar rayuwa a matsayin daya daga cikin dalilan da zai sa jihohin su fuskanci yunwa. Da ma dai bankin na duniya a wani rahoto ya ayyan...