Skip to main content

Ko shigar da abinci Najeriya zai samar da mafita ga tsadar rayuwa?

Ake ciki sannan dan kasuwa shi ma yana fuskantar koma-bayan ciniki saboda mutane na fama wajen samun kudin da za su shiga kasuwa.

Ya ce tsugunu ba ta kare ba a damar da gwamnati ta bayar na ba da dala ga duk mai son shigar da abinci daga wasu kasashen kasancewar dalar ta yi karanci a babban bankin Najeriya.

"Domin duk wanda zai siyo abinci a waje, ko dai ya canza naira zuwa dala, ko naira zuwa CFA, ko zuwa me ka canza naira, idan ka siyo abincin ba za ka sayar da shi a kan sauki ba." in ji Dr Kani.

Dr Muhammad Suleiman Kani ya ce matukar gwamnati na son kawo sauki toh kamata ya yi gwamnati ta haramta shigar da duk kayan da za a iya samu a Najeriya.

A cewarsa, idan gwamnati ta dauki wannan mataki, ya kamata ta hanzarta tayar da komadar kamfanoni da wutar lantarki domin su tsaya da kafafunsu.

Ya kuma yi kira ga shugaban kasa ya tashi tsaye wajen yin abin da ya dace domin fitar da Najeriya daga kangin da take ciki.

A cewar masanin, ya kamata gwamnati ta cika alkawuran da ta daukar wa jama'a bayan janye tallafin man fetur na kara albashi da inganta walwalar al'umma da tayar matatar mai ta Fatakwal.

A cewar kwararren kan samar da abinci, tsarin shigar da abinci daga wasu kasashen hanya ce mai kyau sai dai akwai bukatar gwamnati ta sa ido domin tabbatar da cewa tsarin ya tafi sumul kalau ga amfanin yan kasa.

Ya ce "dole hukumomin tsaro su sa ido saboda dabi'ar yan Najeriya, za a iya shigar da kayan abincin sai ka ga wasu tsirarun mutane sun debe abincin an sauya buhu, sun kai shi kasuwa ana kuma cinikinsa."

Ya kuma ce bai kamata gwamnati ta sake kuskuren bayar da abincin ta hannun gwamnoni ba, kasancewar irin wannan tsarin a baya, bai yi nasara ba.

Dr Kani ya ce a yi amfani da kasuwannin da ake da su da kuma cibiyoyin gwamnati na harkar abinci, sannan a yi tsarin a bude, "babu maganar gwamnoni ko yan majalisa."

Ya ce gwamnati ta aiwatar da abin da kanta sannan ta saka yan farar hula da za su sa ido kan yadda tsarin ke tafiya domin tabbatar da an yi shi bisa gaskiya.

Dr Muhammad Kani ya bayyana cewa tsarin na gwamnati zai iya shafar harkokin yan kasuwa inda ya ce a wasu kasashe kamar Amurka gwamnati tana siyan kayan abinci sai ta rage farashinsu a duk lokacin da aka gama harkokin noma.

Ya ce tsarin bai tsaya iya nan ba, Saudiyya ma tana aiwatar da irin tsarin.

"A Saudiyya, akwai lokacin da idan kaya suka yi yawa sai ta gayyato manoma, ta ce kada su yi noma," tana tambayar nawa ce ribarsu sai ta dauki ribar ta basu.

"Saboda idan ya yi yawa ya wuce hankali za a yi asara, za ku noma ba ku ci riba ba." kamar yadda ya ce.

A cewar masanin, daukan wannan tsarin zai kawo gasa kuma zai sa wadanda suke samar da abin na cikin gida suma su karyar da farashin kayansu.

Masanin ya ce rashin isassun rumbuna ka iya kawo tarnaki ga matakin shigo da kayan abincin saboda rashin tanadin wuraren da za a ajiye su wanda hakan zai iya jawo lalacewarsu.

Ya kuma a yanzu gwamnatin ba ta da kayan abincin a kasa, a yanzu ne za ta shigo da su kuma abin tambayar a cewarsa shi ne da wane kudi za ta siyo kayan?

Ya ce ma'ana dole sai gwamnati ta ciwo bashi domin sayo kayan abincin.

AMH Hausa 

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Kuskuren Farko da Tinubu Yayi Ya Jefa Mutanen Najeriya a Wahala.

Tsohon shugaban PACAC, Itse Sagay ya soki gaggawan janye tallafin man fetur da aka yi a bara Farfesan yana gani kyau sabon shugaban Najeriya ya jira sai matatun cikin gida sun fara aiki tukun Itse Sagay yana sa ran gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kawo sauyin al’amura a Najeriya  - Itse Sagay Farfesa ne kuma babban lauya a Najeriya, ya soki tsarin janye tallafin man fetur da aka tabbatar da shi a 2023. A wata zantawa da tashar Channels tayi da shi, Farfesa Itse Sagay ya yi tir da da Bola Tinubu a kan daina biyan tallafin man fetur.  Itse Sagay ya bada misali da matatar Aliko Dangote da ta gwamnati da ke Fatakwal, ya so ina ma sun fara aiki kafin fetur ya tashi. Itse Sagay bai ji dadin tashin fetur ba "Fetur yana da muhimmanci a rayuwarmu.  Tsadar rayuwa ta na ta karuwa kuma rayuwa tayi kunci. Ina tunani ya kamata a ce mun jira na watanni shida domin za a fara tace mai a gida, sai a cire tallafi. Gaggawa da yadda aka janye tallafin nan ta ke ya kirkiro wahalar...