Skip to main content

Kuskuren Farko da Tinubu Yayi Ya Jefa Mutanen Najeriya a Wahala.

Tsohon shugaban PACAC, Itse Sagay ya soki gaggawan janye tallafin man fetur da aka yi a bara Farfesan yana gani kyau sabon shugaban Najeriya ya jira sai matatun cikin gida sun fara aiki tukun Itse Sagay yana sa ran gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kawo sauyin al’amura a Najeriya 

- Itse Sagay Farfesa ne kuma babban lauya a Najeriya, ya soki tsarin janye tallafin man fetur da aka tabbatar da shi a 2023. A wata zantawa da tashar Channels tayi da shi, Farfesa Itse Sagay ya yi tir da da Bola Tinubu a kan daina biyan tallafin man fetur. 

Itse Sagay ya bada misali da matatar Aliko Dangote da ta gwamnati da ke Fatakwal, ya so ina ma sun fara aiki kafin fetur ya tashi. Itse Sagay bai ji dadin tashin fetur ba "Fetur yana da muhimmanci a rayuwarmu. 

Tsadar rayuwa ta na ta karuwa kuma rayuwa tayi kunci. Ina tunani ya kamata a ce mun jira na watanni shida domin za a fara tace mai a gida, sai a cire tallafi. Gaggawa da yadda aka janye tallafin nan ta ke ya kirkiro wahalar da kusan da kyar ake rayuwa.

Daily Trust ta ce Sagay bai goyon bayan yadda ake tafiyar da abubuwa a yau, ya sha bam-bam da gwamnatin da aka rantsar a bara. 

Dole Shugaba Tinubu ya ceci Naira 

A hirar da aka yi da shi, lauyan ya ce dole sai an yi hobbasa domin a ceci Naira wanda kullum ta ke kara rasa daraja a kan Dala. Ko a mafarki, Farfesan bai taba tunanin za a zo lokacin da za a canji Dalar Amurka a kan N1, 000, sai dai yana sa ran za a kawo gyara. 

Gwamnatin Tinubu ta jawo tsadar fetur 

A dalilin janye tallafi da gwamnati tayi, ana da labarin farashin litar man fetur ya tashi daga N190 zuwa kusan N700 a fadin kasar. Kwanaki an yi ta rade-radin fetur zai kara kudi, zancen da gwamnati ta karyata, ta kuma nuna ba a dawo da biyan tallafin man ba.

AMH HAUSA 

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Abubuwan da suka haifar wa duniya tsadar Rayuwa

Tsadar rayuwa wata matsala ce da ke neman zame wa duniya wata babbar barazana. Inda ƙasashen duniya da dama ke cikin wannan matsala, sakamakon tashin farashin abubuwan amfani na yau-da-kullum. A baya-bayan nan Najeriya da sauran ƙasashen Afirka irinsu Ghana da Nijar na fuskantar matsalar tsadar rayuwa. To sai dai matsalar ba ta tsaya ga nahiyar Afirka kaɗai ba, al'amari ne da ya shafi duniya baƙi-ɗaya. Shin me ke haifar da wannan matsala da tsadar rayuwa a faɗin duniya? 1-Tashin farashin makamashi da man fetur An samu ƙaruwar farashin man fetur tun bayan ɓarkewar annobar korona, inda buƙatar man fetur ɗin ta ƙaruwa a duniya sakamakon matakin kullen korona da ƙashen duniya da dama suka ɗauka. Wannan abu ya sa man fetur ɗin ya kai tsadar da bai taɓa kai wa ba cikin shekaru masu yawa. A yanzu dai ana sayar da gangar ɗanyen mai man fetur kan dala 79 zuwa sama a kasuwannin duniya. Hakan ya faru ne sakamakon yaƙin Ukraine da Rasha, Ita dai Rasha na cikin ƙasashen da suke da arzikin man f...