Skip to main content

Jihohin arewacin Najeriya bakwai da za su fuskanci yunwa

-Bankin Duniya

A wani rahoto da bankin na duniya ya wallafa tun ranar 1 ga watan Fabrairu kuma ya samu watsuwa a ranar 8 ga watan na Fabrairu ya fitar da bayan na sassan duniya da matsalolin yunwa da za su fuskanta.

A sashen Afirka ta yamma da ta tsakiya, rahoton mai taken 'Food Security Update 2024', ya bayyana cewa wasu jihohi guda bakwai na arewa maso yammaci da gabashi da wadanda za su fuskanci matsalar yunwa tun daga farkon shekarar nan har zuwa watan Mayu.
Jihohin dai su ne:
Adamawa
Borno
Kaduna
Katsina
Sokoto
Yobe
Zamfara.
Rahoton dai ya bayyana dalilan rashin tsaro na 'yan bindiga da ke satar jama'a a jihohi kamar Kaduna da Katsina da Sokoto da Zamfara, inda su kuma Borno da Yobe da Adamawa ke fuskantar matsalar Boko Haram.

Harwayau, rahoton ya yi wa jihohin kudin goro da sauran sassan Najeriya da ke fama da matsalar tsadar rayuwa a matsayin daya daga cikin dalilan da zai sa jihohin su fuskanci yunwa.
Da ma dai bankin na duniya a wani rahoto ya ayyana Najeriya a matsayin kasa ta 6 a jerin kasashen da suka fi talauci har Mutane na shan ruwan zafi saboda yunwa a Najeriya'

Wadanne matakai za a bi domin rage radadin yunwa?

Masana na cewa matakan iri biyu ne wato na gajere da dogon zango:

Gajeren zango:

Dr Mohammed Sulaiman Kani masani kan tattalin arziki da samar da abinci kuma malami a kwalejin ilimi ta tarayya da ke Kano ya ce dole ne gwamnonin jihohin da abin ya shafa su bude rumbunan abinci na jihar su fito da kayan abinci a sayar a kan farashi mai rahusa.

Masanin ya kara da cewa "dole ne a yi kokarin samar da kwarkwaryar tsaro ga mutanen yankunan domin samun damar yin noma."
Dogon zango:

Dangane kuma da matakai na dogon zango, masanin ya lissafa abubuwa guda hudu:
Tsaro
Noma
Samar da wutar lantarki
Tabbatar kamfanonin cikin gida sun tashi
"Idan dai har gwamnati ba za ta tabbatar da wadannan abubuwan ba to fa a rahoton bankin na duniya na nan gaba za a iya ganin sunayen wasu jihohin sabbi sun fado cikin yanayin yunwa da talauci,"

 in ji Dr Mohammed Kani.

AMH Hausa 

Popular posts from this blog

Matakan Da Gwamnatin Najeriya Ta Dauka Na Kayyade Farashi Ba Zai Kawar Da Yunwa Ba

Masana tattalin arziki a Najeriya na ganin matakan da gwamnatin kasar ke dauka da kyar za su yi tasiri, idan dai ba an kawo karshen matsalar tsaro da kuma dawo da tallafin man fetur da bude iyakoki domin shigowa da abinci cikin kasar ba. ‘Yan Najeriya, musanman talakawa na ci gaba da kukan tsada da hauhawar kayan masarufi a kasuwannin kasar. Biyo bayan zanga zangar lumana da wasu mata suka jagoranta a jihar Neja da kuma wasu daban da aka gudanar a jihohin Kano da Osun, ya sa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, daukan matakan ba da umarnin fito da tan-tan na abinci da ke runbunan gwamnantin kasar, domin karya farashin kayan masarufi da ke neman ya gagari kundila. To sai dai kuma a cewar wani masanin harkar gona, Farfesa Abubakar Gudigi, na jami’ar Ibrahim Babangida da ke Lapai a jihar Neja, ya ce da sake a wannan dabara ta gwamnati. Gudigi ya ce matakin gwamnati na karya farashi, ba shi zai kawar da yunwa ba, domin yanzu haka akwai wadanda ke sayen kayan abinci a kauyuka, domin sayarwa...

Kuskuren Farko da Tinubu Yayi Ya Jefa Mutanen Najeriya a Wahala.

Tsohon shugaban PACAC, Itse Sagay ya soki gaggawan janye tallafin man fetur da aka yi a bara Farfesan yana gani kyau sabon shugaban Najeriya ya jira sai matatun cikin gida sun fara aiki tukun Itse Sagay yana sa ran gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta kawo sauyin al’amura a Najeriya  - Itse Sagay Farfesa ne kuma babban lauya a Najeriya, ya soki tsarin janye tallafin man fetur da aka tabbatar da shi a 2023. A wata zantawa da tashar Channels tayi da shi, Farfesa Itse Sagay ya yi tir da da Bola Tinubu a kan daina biyan tallafin man fetur.  Itse Sagay ya bada misali da matatar Aliko Dangote da ta gwamnati da ke Fatakwal, ya so ina ma sun fara aiki kafin fetur ya tashi. Itse Sagay bai ji dadin tashin fetur ba "Fetur yana da muhimmanci a rayuwarmu.  Tsadar rayuwa ta na ta karuwa kuma rayuwa tayi kunci. Ina tunani ya kamata a ce mun jira na watanni shida domin za a fara tace mai a gida, sai a cire tallafi. Gaggawa da yadda aka janye tallafin nan ta ke ya kirkiro wahalar...

Abubuwan da suka haifar wa duniya tsadar Rayuwa

Tsadar rayuwa wata matsala ce da ke neman zame wa duniya wata babbar barazana. Inda ƙasashen duniya da dama ke cikin wannan matsala, sakamakon tashin farashin abubuwan amfani na yau-da-kullum. A baya-bayan nan Najeriya da sauran ƙasashen Afirka irinsu Ghana da Nijar na fuskantar matsalar tsadar rayuwa. To sai dai matsalar ba ta tsaya ga nahiyar Afirka kaɗai ba, al'amari ne da ya shafi duniya baƙi-ɗaya. Shin me ke haifar da wannan matsala da tsadar rayuwa a faɗin duniya? 1-Tashin farashin makamashi da man fetur An samu ƙaruwar farashin man fetur tun bayan ɓarkewar annobar korona, inda buƙatar man fetur ɗin ta ƙaruwa a duniya sakamakon matakin kullen korona da ƙashen duniya da dama suka ɗauka. Wannan abu ya sa man fetur ɗin ya kai tsadar da bai taɓa kai wa ba cikin shekaru masu yawa. A yanzu dai ana sayar da gangar ɗanyen mai man fetur kan dala 79 zuwa sama a kasuwannin duniya. Hakan ya faru ne sakamakon yaƙin Ukraine da Rasha, Ita dai Rasha na cikin ƙasashen da suke da arzikin man f...